SiyasaAfirka
Kasashen AES sun yi kiranye ga jakadunsu na kasar Aljeriya
April 7, 2025Talla
Shugabannin mulkin sojin kasashen Mali da Burkina Faso da Jamhuriyar Nijar sun yi kiranye ga jakadun kasashensu da ke Aljeriya tare kuma da yanke huldar diflomasiyya da kasar, bayan kakkabo jirgi mara matuki mallakin kasar Mali da Aljeriya ta yi.
Karin bayani: Mali ta soke yarjejeniya da 'yan tawayen Abzinawa
Firaministan Mali Janar Abdoulaye Maiga ya yi watsi da zargin da Aljeriya ta yi na cewa jirgin ya keta ta sararin samaniyar kasarta, ta la'akari da dokokin kasa da kasa. Janar Maiga ya kara da cewa matakin Algiers na nuna cewa kasarta na goyon baya tare da daukar nauyin ayyukan ta'addanci.