SiyasaJamus
Jamus ta watsa mana kasa a ido bayan janye tallafin makamai
August 12, 2025Talla
Jakadan ya furta hakan a yayin tattaunawa da gidan talabijin na Welt, inda ya kara da cewa gwamnatin Jamus kamata yayi ta hana kungiyar Hamas mallakar makamai ba wai ta hana Isra'ila amfani da makamai ba.
Jakadan ya kara da cewa matakin Berlin ka iya shafar dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu, kuma babu shakka matakin Jamus zai faranta wa kungiyar Hamas.
Karin bayani: Jamus da wasu kasashe na ci gaba da jefa kayan agaji a Gaza
Tun da fari dai shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya sanar da dakatar da tallafin makamai ga Isra'ila domin ci gaba da kai hare-hare Zirin Gaza.